Hare-haren Boko Haram na kara yin kamari
December 20, 2018Talla
Mutane da dama ne dai aka ba da rahoton cewar sun rasa rayukansu a cikin 'yan kwanakin baya-baya nan a sakamakon hare-haren da Kungiyar Boko Haram ke ci gaba da kai wa a kasashen Najeriya da Nijar da Chadi da kuma Kamaru a ciki kuwa har da sojoji. Wadannan hare-hare na faruwa ne duk da irin matakan tsaro da ksashen ke tanada.