1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran na bitar shawarwarin EU

Abdul-raheem Hassan
August 8, 2022

Kungiyar Taryyar Turai ta mika daftarin karshe kan tattaunawar da ake yi na neman farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran da kasashen yamamcin duniya suka cimma a shekarar 2015.

https://p.dw.com/p/4FHiB
Österreich Burgenland | Treffen zu Iran Atomabkommen
Hoto: EU Vienna Delegation/AA/picture alliance

Iran ta ce tana sake bitar shawarwarin da aka tsayar don ceto yarjejeniyar ta nukiliya aka cimma a 2015 da kasahen yammacin duniya, bayan da kungiyar Tarayyar Turai ta gabatar da kundin karshe na tattaunawar ceto yarjejeniyar a ranar Litinin.

A ranar Alhamis ce kasashen Biritaniya da Chaina da Faransa da Jamus da Iran da Rasha da kuma Amirka suka sake komawa teburin tattaunawa a Vienna, watanni bayan dakatar da batun.