1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaba da rigakafin AstraZeneca a Jamus

Abdul-raheem Hassan
March 19, 2021

Gwamnatin tarayyar Jamus za ta gana da masu ruwa da tsaki na jihohin kasar 16 don maida hankali kan gangamin allurar rigakafin corona da ke shan suka kan yadda aikin ke tafiyar hawainiya.

https://p.dw.com/p/3qqWK
Weltspiegel 18.03.2021 | Corona | AstraZeneca-Impfstoff
Hoto: Dado Ruvic/REUTERS

Matakin na zuwa ne bayan da hukumar tantance sahihancin magunguna ta Kunguyar Tarayyar Turai ta cimma mastaya kan tabbatar da ingancin rigakafin kamfanin AstraZeneca bayan gudanar da bicnike kan zargin illarsa a kan jama'a.

Yanzu haka dai kasashe da dama na duba yiwuwar ci gaba da amfani da allurar astraZeneka bayan samun tabbacin ingancinsa kwanaki kadan bayan da kaashen duniya da dama suka dakatar da amfani da allurar saboda zargin tana daskarar da jinin wadanda aka fara yi wa.