Bazuwar murar tsuntsaye a Najeriya
February 20, 2006Talla
Gwamnatin Najeriya ta bada tabbacin bazuwar cutar murar tsuntsaye zuwa wasu jihohin arewacin kasar 3 kuma,wanda a yanzu ya kawo yawan jihohi da cutar ta bulla zuwa jihohi 7 a Najeriyar.
Ministan yada labarai,Frank Nweke,ya fadawa manema labarai cewa ya zuwa yanzu dai jihohin Kano,Kaduna;Plateau,Bauchi,Katsina da Zamfara da kuma babban birnin taraiya Abuja an samu tabbacin isar kwayar cutar ta murar tsuntsaye.