Bam ya halaka rayuka a Najeriya
January 7, 2020Talla
Akalla mutum 30 ne suka mutu yayin da wasu suka jikkata, sakamakon tashin da wani bom ya yi a wani bangare na jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriyar.
Shaidu sun ce lamarin wanda ya faru a kan wata kasuwa mai cunkoson jama'a a garin Gamboru, ya ma shafi wani bangare na garin Fotokol na Jamhuriyar Kamaru da ke iyaka da Najeriya.
Sabbin alkaluma na cewa mutum 35 ne suka jikkata a tashin bom din hadin gida da ya auku da la'asariyar jiya Litinin.
Wasu jami'an sa kai sun tabbatar da tashin bom din, duk da cewar hukumomi ba su shaida wa kamfanin dillancin labaran Reuters ba da yammacin na Litinin.
Kungiyar Boko Haram mai gwagwarmaya da makamai dai ta yi kaurin suna wajen kai hare-hare a jihar Borno da Yobe da kuma jihar Adamawa a Najeriyar.