1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Jagoran 'yan adawa ya ayyana lashe zaben Kamaru

Suleiman Babayo MA
October 14, 2025

Issa Tchiroma Bakary wanda ke zama jagoran 'yan adawa na kasar Kamaru, ya bayyana lashe zabe shugaban kasa da aka gudanar ranar 12 ga watan Oktoba, inda ya nemi Shugaba Paul Biya ya rungumi kaddara.

https://p.dw.com/p/51yZj
Issa Tchiroma Bakary jagoran 'yanadawa na kasar Kamaru
Issa Tchiroma Bakary jagoran 'yanadawa na kasar KamaruHoto: Daniel Beloumou Olomo/AFP

Jagoran 'yanadawa na kasar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar ranar Lahadi da ta gabata 12 ga watan Oktoba da muke ciki.

Matsayin jagoran 'yan adawa

Issa Tchiroma Bakary jagoran 'yanadawa na kasar Kamaru
Issa Tchiroma Bakary jagoran 'yanadawa na kasar KamaruHoto: Welba Yamo Pascal/AP Photo/dpa/picture alliance

A cikin wani jawabi da ya gabatar Tchiroma Bakary ya bukaci ganin an mutunta zaben da 'yan kasa suka yi.

Mai shekaru 76 da haihuwa Tchiroma Bakary ya bukaci Shugaba Paul Biya ya rungumi kaddara na faduwa a zabe. Shi dai jagoran 'yan adawan ya shafe shekaru da dama a matsayin minista a gwamnatin ta Biya.

Shugaba Paul Biya na Kamaru
Shugaba Paul Biya na KamaruHoto: Henri Fotso/DW

Zai dauki makonni biyu kafin sanin sakamakon zaben kasar ta Kamaru inda Shugaba Biyu mai shekaru 92 kuma wanda ya fi kowanni shugaba a duniya tsufa, yake neman fadada mulkin na tsawon shekaru 43 da wani sabon wa'adin mulkin shekaru bakwai, a wa'adi na takwas.