Horst Seehofer ya yi tsokaci a kan kisan wani dan siyasa
June 18, 2019Talla
A halin da ake ciki 'yan sanda na tsare da wani mutumin da ake zargi wanda ya taba kai hari a wani sansanin 'yan gudun hijira a shekara ta 1993 dan jam'iyyar NPD, ta masu ra'ayin 'yan Nazi. Mutumin da aka kashen Walter Lübcke dan kimanin shekaru 65 da haifuwa an taras da gawarsa a kan filin gidansa a Wolfhagen da ke cikin Jihar Hessen da ke a yankin tsakiya maso yammaci na Jamus a farkon wannan wata na Yuni. Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi Allah wadai da harin da ta ce abin takaici ne.