1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An daure dan gudun hijira kan kisa a Jamus

Abdul-raheem Hassan
September 3, 2018

Kotun Jamus ta yanke wa dan gudun hijira hukuncin dazrin shekaru takwas da rabi, bayan samunshi da laifin kashe tsohuwar budurwarsa. Wannan ya zo a daidai lokacin da ake zanga-zangar kin jinin baki a birnin Chemnitz.

https://p.dw.com/p/34E5X
Urteil im Mordprozess von Kandel
Hoto: DW/R. Staudenmaier

An yanke hukuncin ne a wata kotu a birnin Landau da ke Kudu maso yammacin Jamus. sai dai babu karin bayani kan dan gudun hijiran Abdul D, sai dai wasu bayanai na danganta wanda ya aikata kisan da dan kasar Afganistan da ke neman mafakar siyasa a Jamus.

Hukuncin ya zo ne a daidai lokacin da ake kokarin kwantar da zanga-zangar nuna kin jinin baki a garin Chemnitz da ke gabashin kasar bayan da wasu 'yan gudun hijira biyu suka kashe Bajamushe da wuka.

Dama dai kasar na cikin rudani kan tsarin bude kofa ga dubban 'yan gudun hijira, inda ko a baya-bayannan sai da aka samu rarrabuwar kawuna a cikin jam'iyyun hadaka da ke mulki kan batun 'yan gudun hijira.