1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta kara yawan dakarunta a Jamus

April 15, 2021

Sakataren harkokin wajen Amirka Lloyd Austin a wata ziyara da ya kawo jiya a nan Jamus, ya ce Amirka za ta kara yawan dakarunta a kasar ta Jamus.

https://p.dw.com/p/3ryOX
Deutschland US-Verteidigungsminister Lloyd Austin und Annegret Kramp-Karrenbauer
Hoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Lamarin kara yawan dakarun ya yi hannun riga da kudurin tsohon shugaban kasar Donald Trump da ya kuduri zabge yawan dakarun. Sanarwar hakan ta biyo bayan ganawar da sakataren ya yi da ministar harkokin tsaron Jamus Annegret Kramp-Karrenbauer a birnin Birlin, kuma a dai dai lokacin da kasar ta Amirka ta bayar da sanarwar janyen dakarunta a Afghanistan nan da 11 ga watan Satumbar wannan shekarar. Matakin da Amirkar ta dauka na kara yawan dakarunta a Jamus, wata hanya ce ta sake farfadowa da kyakyawar alaka tsakanin kasashen biyu da ma sauran kasashe mambobin kungiyar tsaro ta NATO.