1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka da China sun amince da rage gurbata yanayi

Suleiman BabayoSeptember 3, 2016

Amirka da China sun amince da yarjejeniyar rage iska mai gurbata yanayi.

https://p.dw.com/p/1JvK5
China Hangzhou Barack Obama und Xi Jingping bei G20 Klimagipfel
Hoto: Getty Images/AFP/H. Hwee Young

Shugaba Barack Obama na Amirka da Shugaba Xi Jinping na kasar China sun amince da fara aiki da yarjejeniyar birnin Paris na kasar Faransa kan rage fitar da iska mai gurbata yanayi. A wannan Asabar shugabannin kasashen biyu da suke kan gaba wajen fitar da iskar mai gurbata sararin samaniya suka tabbatar da haka yayin da China ta fara tarbar shugabannin kasashen masu kafin arziki na duniya karkashin kungiyar G20.

Matakin kasashen na Amirka da China ya tabbatar da ceqa zuwa karshen wannan shekara za a fara aiki da yarjejeniyar ta birnin Paris, da za ta taimaka wajen rage dumamar yanayin duniya.

Tuni babban jami'in Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ya nuna jin dadi da wannan matakin na kasashen Amirka da China.