An samu tashin hankali a wasu Jihohin Najeriya
February 23, 2019Talla
Hadin gwiwar wasu kungiyoyin farar hula masu saka ido a zaben Najeriya, sun ce an kashe mutane 16 a wasu Jihohi guda takwas na kasar, amma dai duk da haka zaben na ci gaba da gudana. Kungiyoyin sun ce daga cikin Jihohin da aka samu tashin hankalin har da Jihar Lagos inda aka hana wa wasu jama'ar jefa kui'a, abin da ya sa wasu 'yan daba suka cinawa kuri'un wuta. Haka ma a yankin kudu maso gabashin Najeriya a yankin Naija Delta an samu barkewar tashin hankali.