Za a fara shari'ar 'yan Boko Haram a Najeriya
October 9, 2017Talla
An dai bayyana gabatar da mutanen ne ba tare da inda jama'a suka sani ba, kazalika an yi niyar haramta wa 'yan jaridu da kungiyoyi halartar zaman shari'ar da za a fara a wannan Litinin.
Wadanda ake zargi da ayyukan ta'addancin da za a gabatar da su gaban kuliya, suna a tsare sama da shekaru takwas tun bayan bullar kungiyar Boko Haram. A yanzu ana zargin mutanen da haddasa asarar rayuka akalla fararen hula da jami'an gwamnati sama da dubu 20 a yakunan Arewa maso Gabashin Najeriya.
Wata kididdigar hukuma ta nuna cewa gabannin shari'ar da za a fara a wannan Litinin, mutane tara ne kadai aka yankewa hukunci a cikin mutane 13 da suka fuskanci shari'a a kan zarginsu da ayyukan kungiyar ta Boko Haram.