'Yan fashin teku sun sace Turkawa 15
January 24, 2021Talla
Hukumomin kula da jiragen ruwan Turkkiyya sun ce ma'aikatan jirgin sun killace kansu a boyayyen wuri amma sai dai 'yan fashin suka balla wurin bayan kwashe sa'a shida suna fama, barayin sun bar jirgin a tekun Guinea da wasu ma'aikatan jirgin uku a cewa kafanin yada labaran Turkiyya Anadolou.
Gabar tekun Guinea da na Najeriya da Togo da Benin da Kamaru, na su ne gabar teku mafi hatsari na 'yan fashi a duniya a cerwa hukumar kula da teku na kasa da kasa. Ko a 2019, sai dai 'yan fashin tekun Najeriya suka yi garkuwa da Turkawa 10.