1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Wasu dalilan tabarbarewar ilimi a Najeriya

July 1, 2021

Dalibai masu neman shiga jami'o'i a Najeriya sun yi mummunar faduwa a bana, bayan rubuta jarrabawar neman shiga manyan makarantun da aka saba yi a duk shekara.

https://p.dw.com/p/3vt5b
Nigeria Abuja 2014 | Studenten & Ergebnis der Prüfungen
Hoto: Imago Images/Xinhua Afrika

Masana da masu fashin baki kan harkokin ilimi na ci gaba da bayyana irin yadda ilimi ke kara tabarbarewa musamman ma a arewacin kasar. 

Dalilai da dama ne dai suka sanya daliban rashin katabus a banan, wadanda suka hada da rufe makarantu da aka yi saboda gudun yaduwar cutar COVID-19. Haka ma akwai wadanda ke ganin maida hankali da matasa ke yi a shafukan sada zumunta na zamani maimakon karatu yadda ya dace. Faduwar dai ta yi munin da ba a taba ganin irinta ba a kasar.