1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Turkiyya na bincike kan mutuwar 'dan jarida

Zulaiha Abubakar
October 21, 2018

Masu gabatar da kara a kasar Turkiyya sun gayyaci wasu sabbin shaidun a ci gaba da binciken da gwamnatin kasar ke yi kan mutuwar 'dan jaridar nan Jamal Kashoggi.

https://p.dw.com/p/36uIe
Dschamal Chaschukdschi
Hoto: Getty Images/AFP/M. Al-Shaikh

Bayan da kasar Saudi Arabiya ta tabbatar da rasuwar 'dan jaridar a ofishin jakadancin ta da ke birnin Istanbul kakakin jam'iyyar AKP mai mulki a Turkiyya, ya bayyana cewar gwamnatin kasar ba ta da niyyar dora alhakin wannan mummunan al'amari a kan wani to amma fa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen bayyana abin da ya faru a fili ba.