1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Yada tsohon bidiyo ya tayar da rikici a Abidjan

Ramatu Garba Baba
May 21, 2021

Mutum guda ne ya mutu a yayin wani rikici da ya barke a Abidjan a tsakanin wasu 'yan kasar Cote d'Ivoire da 'yan Nijar da ke zaune a a babban birnin kasar.

https://p.dw.com/p/3tnJy
Elfenbeinküste | Präsidentschaftswahlen | Ausschreitungen in Abidjan
Hoto: Issouf Sanogo/AFP/Getty Images

Binciken da aka gudanar bayan aukuwar lamarin, ya nuna cewa, wani tsohon bidiyo da ya karadde shafukan sada zumunta na zamani a ranar Larabar da ta gabata, da a ciki ya nuna yadda wasu da aka ce jami'an tsaron Nijar ne, na gallazawa wa wasu matasa 'yan Cote d'Ivoire, ya zama dalilin fadan da ya raunata wasu sama da dari baya ga asarar tarin dukiya.

Ana ganin an nadi bidiyon a Nijar tun a shekarar 2019. Ba a dai kai ga tantance sahihancin bidiyon ba. Gwamnatin kasar Cote d'Ivoire ta yi Allah-wadai da lamarin da ya kawo wannan rudanin, inda ta nemi a zauna lafiya. Tuni aka kaddamar da bincike bayan kama wasu kimanin ashirin da ake wa tambayoyi. Kasar da ta kasance a sahun gaba a noman Koko a duniya, ta bar kofofinta a bude ga masu son aiki a gonakin kokon, jamhuriyar Nijar na daya daga cikin kasashen yankin da 'yan kasar ke shiga don neman abin yi.