1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsageru za su koma ta'adi a Najeriya

November 3, 2017

'Yan bindigar yankin Naija Delta mai arzikin mai a Najeriya sun ce tsagaita buda wuta da suka yi kan bututan mai, ya zo karshe.

https://p.dw.com/p/2myR1
Nigeria Ölrebellen
Hoto: Getty Images/AFP/P. Utomi Ekpei

Mayakan tarzoma a yankin Naija Delta mai arzikin mai a Najeriya sun ce tsagaita buda wuta da suka yi kan bututan mai, ya zo karshe. Wata sanarwar da suka wallafa a shafin Intanet a wannan Juma'ar, kungiyar ta Niger Delta Avengers, ta ce rijiyoyin mai da ke yankin za su fara fuskantar hare-hare.

Kasar ta Najeriya dai ta ji a jikinta ashekarar da ta gabata, sakamakon hare-haren da mayakan kungiyar suka sha kaddamarwa kan cibiyoyin mai da ke yanki kudancin kasar. Hare-haren nasu dai sun kaiga rage man da kasar ke hakowa matuka, wanda ba a sake ganin irinsa ba kimanin shekaru 30 da suka gabata.