1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump: za a hana 'yan Najeriya shiga Amirka

Zulaiha Abubakar
February 1, 2020

Shugaba Donald Trump na Amirka ya umarci  haramta wa 'yan cirani daga kasashen Najeriya da Myanmar da Iritirya da Krygystan da Sudan da kuma Tanzaniya shiga kasar sakamakon tabarbarewat tsaro a kasashen .

https://p.dw.com/p/3X8Rn
Weltwirtschaftsforum 2020 in Davos | Donald Trump, Präsident USA
Hoto: picture-alliance/AP Photo/E. Vucci

Gwamnatin Amirka ta kebe ranar 22  ga wannan wata na Fabrairu a matsayin ranar da wannan tsari zai fara aiki kamar yadda hukumar shige da ficen kasar ta sanar. Wannan sabon tsari na zuwa ne gabanin zaben da kasar za ta gudanar a bana, shekaru uku bayan shugaba Trump ya haramta wa wasu kasashe shiga Amirka. Al'amrin da ya haifar da cece-kuce.

Tun bayan hawan sa mulki shugaban na Amirka ya tsaurara wa wasu kasashe da suka hada da kasashe 'yan rabbana ka wadata izinin shiga Amirka. sai da kasar Tantaniya ta mayar da martanin cewar Amirka ba ta sanar da ita a hukumance ba don haka ba ta da masaniya.