1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron AU kan tsaro da Ebola a Afirka

Ahmed SalisuJanuary 30, 2015

Taron shugabannin kasashen Afirka na shekara-shekara na wannan karon zai maida hankali kan kalubalen tsaro a Najeriya da kuma cutar nan ta Ebola a Afirka.

https://p.dw.com/p/1ETFI
Nkosazana Dlamini-Zuma
Shugabar kungiyar kasashen Afrika ta AU Nkosazana Dlamini-ZumaHoto: picture-alliance/dpa/ Y.Valat

Gabannin taron na yau dai, shugabar kungiyar ta AU Nkosazana Dlamini-Zuma ta yi kiran hada karfi a karfe wajen dakile aiyyukan masu kaifin kishin addini da ke cin karensu ba babbaka a wasu kasashen nahiyar.

Tuni dai kwamitin tsaro da zaman lafiya na AU din ya bukaci a samar da wata rundunar soji mai yawan dakaru dubu 7 da dari 5 domin kawo karshen tada kayar bayan 'yan bindiga.