1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tallafin ƙasashen duniya ga Mali

May 16, 2013

Tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a Mali, ƙasar ta shiga wani yanayi na rashin tsaro, amma yanzu ƙasashen duniya sun sa baki wajen samar mata kyakyawar makoma.

https://p.dw.com/p/18ZYL
French President Francois Hollande (C) poses for a family photo with European Commission President Jose Manuel Barroso (R) and Mali's interim President Dioncounda Traore at the donors' conference on the development of Mali in Brussels May 15, 2013. International donors pledged more than 3.25 billion euros ($4.22 billion) on Wednesday to help Mali recover after a conflict with al Qaeda-linked Islamists, Hollande said. REUTERS/Laurent Dubrule (BELGIUM - Tags: POLITICS BUSINESS)
Hoto: Reuters

An yi ta ɗora alhakin rikicin Mali kan Abzinawan ƙasar, inda 'yan tawaye su ka yi amfani da damar hargitsin suka nemi aiyana yankin arewacin ƙasar a matsayin 'yantacciyar ƙasa. A watan Janairu bayan da Faransawa suka tura dakarunsu waɗanda suka haɗa gwiwa da dakarun Mali da na Afirka, sun yi nasarar fitar da 'yan tawayen daga arewacin ƙasar. Sai dai har yanzu akwai rahotannin hare-hare musamman a birnin Gao.

A yanzu haka dai, ƙasashe sun fara baiwa ƙasar tallafi domin ta sake gina kanta, ta kuma daidaita lamuran tsaro.

A ƙasa mun yi muka tanadin rahotanni daban daban kan halin da ake ciki a ƙasar ta Mali