1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masu hannu da shuni sun kuduri aniyar taimaka wa Mali ta fita daga halin kunci

May 14, 2013

A wannan Laraba, gamayyar kasa da kasa ke shirya taro na mussamman a birnin Brussels na Beljiyam, domin tattara kudaden sake gina kasar Mali wadda yanzu haka ke fama da tashe-tashen hankula

https://p.dw.com/p/18XXj
France's President Francois Hollande (L) is welcomed by Mali's interim president Dioncounda Traore upon his arrival at Sevare, near Mopti, on February 2, 2013. President Francois Hollande visits Mali as French-led troops work to secure the last Islamist stronghold in the north after a lightning offensive against the extremists. Hollande will head to Timbucktu and Bamako. AFP PHOTO / PASCAL GUYOT (Photo credit should read PASCAL GUYOT/AFP/Getty Images)
Francois Hollande da Dioncounda TraoreHoto: Pascal Guyot/AFP/Getty Images

Wannan babban taro da zai hada wakilan kasashe masu hannu da shuni da kuma kungiyoyin bada agaji na kasa na kasa, na da burin tattara akalla tsabar kudi Euro miliyan dubu biyu, wanda za a amfani da su wajen sake gina yankin arewacin Mali da yaki ya kacencana, da kuma tabbatar da tsaro cikin kasar.

A ganawar da aka yi makon da ya gabata, tsakanin shugabar Gwamnatin Jamus da shugaba Mahamadou Issoufou na Jamhuriyar Nijar, Merkel ta jaddada mahimmancin hada wannan kudade domin taimakawa Mali.Taron na birnin Brussels zai wakana a daidai lokacin da dakarun gwamnatin Mali suke darkakawa zuwa yankin Kidal, wanda ke cikin hannun kungiyar tawayen MNLA ta abzinawa.

A cewar Ulrich Delius shugaban dake kula da sashen Afrika a Kungiyar Kare hakkokin jama'ar dake cikin baraza wato GfbV wadda ke da cibiyarta a Jamus, ya baiyana zullumin sojojin su wuce gona da iri a kokarinsu na kwatar Kidal daga kungiyar MNLA.

"Mun zuba ido muga yadda sojojin Mali zu su kaddamar da gwagwarmayar kwatar Kidal, za su kiyaye hakkokin abzinawa wanda ba su dauki makamai ba,ko kuma za su gama jiji da jar kanwa.A gaskiya muna cikin zullumi."

French Foreign Affairs Minister Laurent Fabius (R) speaks with Mali president Dioncounda Traore during the international donor conference on Mali at the African Union (AU) headquarters on January 29,2013 in Addis Ababa. The donor conference opened today to drum up funds and troops to help the military operation against Islamist militants in Mali. AU Peace and Security Commissioner Ramtane Lamamra said Monday the African-led force for Mali (AFISMA) will cost $460 million, with the AU promising to contribute an 'unprecedented' $50 million for the mission and Mali's army. AFP PHOTO/SIMON MAINA (Photo credit should read SIMON MAINA/AFP/Getty Images)
Hoto: Simon Maina/AFP/Getty Images

A watan Maris na shekara 2012 kungiyar MNLA ta karbi yankin Kidal kamin daga bisani Kungiyoyin MUJAO da Ansar-Deen su kore su.

Sun sake mamaye Kidal bayan da sojojin Faransa suka fattafaki kungiyoyin masu kaifin kishin addinin Islama daga yankin.

Sojojin Mali sun kuduri aniyar sake kwatar Kidal, domin tabbatar da tsaro cikin kasar kamin zaben shugaban kasa na watan Juli nan wanan shekara.

To saidai a cewar Ulrich Delius abin da kamar wuya Mali ta yi nasara shirya zabe a cikin wannan wa'adi:

"Akwai matsalolin masu yawa tattare da wannan zabe.Misali a halin yanzu, akwai 'yan gudun hijira fiye da dubu dari hudu a kasashen makwafta da kuma wanda ke cikin kasar, cilas suma su yi zabe.

A yanzu babu wani tsari da tanada.Zai wahala a iya shirya zabe watan Juli na wannan shekara" .

Su ma dai kungiyoyin kasa da kasa sun baiyana bukatar ganin Mali ta shirya wannan zabe, domin mika mulki da zabbabiyar gwamnati, to amma a cewar Annette Lohman, shugabar Gidauniyar Friedrich Ebert Stiftung dake birnin Bamako akwai matsaloli biyu da ta kamata taron kasa da kasa na Beljiyam ya fi maida hankali akai:

"Al'umar dake yankin arewacin kasar na cikin kuncin rayuwa.Suna fama da karanci abinci, da karancin asibitoci sannan uwa uba matsalolin tsaro.Kamata tayi a bullo da wani tsari kwakkwara na raya wannan yanki."

©/PANAPRESS/MAXPPP - 05/02/2012 ; ; Mauritania - Malians take refuge in eastern Mauritania, fleeing a new Tuareg rebellion which affect the North of Mali since last January, on February 5, 2012. (Photo Panapress) - Des Maliens se refugient a l'Est de la Mauritanie, fuyant une nouvelle rebellion Touareg qui touche le Nord du Mali depuis janvier dernier. Mauritanie, 5 fevrier 2012. (Photo Panapress)
'Yan dugun hijira daga MaliHoto: picture-alliance/dpa

A nasu gefe,Kungiyoyin kare hakkokin Bani Adama na kasa da kasa, sun bukaci kasashe da kungiyoyi masu hannu da shuni wanda za su taimakawa Mali,su yi la'akari da kare hakkokin Bani Adama, mussamman a daidai wannan lokaci da gwamnatin kasar ta baiyana aniyar kwatar Kidal ta ko wane hali.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Usman Shehu Usman