1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Taliban ta shirya kafa sabuwar gwamnati

September 2, 2021

Jagororin kungiyar Taliban a Afghanistan sun ce nan da dan lokaci kadan ne za su sanar da wadanda za su jagoranci sabuwar gwamnatin da za su kafa a kasar.

https://p.dw.com/p/3zqEf
Afghanistan Kabul - Taliban PK
Hoto: Wakil Kohsar/AFP/Getty Images

Kungiyar Taliban ta ce tana gab da kafa gwamnati a Afghanistan, a daidai lokacin da wasu matan kasar ke zanga-zangar neman yadda sabuwar gwamnatin za ta iya ba su 'yancin yin aiki.

Taliban din dai ta yi alkawarin samar da gwamnati mai sassaucin ra'ayi, sabanin jagorancin da ta yi a tsakanin shekarar 1996 zuwa 2001.

Ana kuma kallon jan aikin da ke a gaban kungiyar, na samar da sauyi a fannin gudanar da al'amura daga matsayin su na mayaka zuwa ga gwamnatin da duniya za ta yi na'am da ita.

A ranar Juma'ar da ke tafe ne dai ake sa ran jagororin na Taliban, za su sanar da sabuwar majalisar ministoci kwanaki kalilan da ficewar Amirka daga kasar.