1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takaddama dangane da zaben gwamnoni

Uwais Abubakar Idris/PAWApril 13, 2015

Tawagar Kungiyar Tarayyar Turai, da ta sa ido a zaben Najeriya ta nuna damuwa a kan karuwar tashe-tashen hankula a zaben gwamnoni, da karancin matan da suka sami nasara.

https://p.dw.com/p/1F7Gt
Nigeria Wahlen Wahlbeobachter
Hoto: DW/Scholz/Kriesch

A rahoton da tawagar Kungiyar Taryyar Turan da ta sa ido a zaben na Najeriya ta gabatar dazu nan a Abuja ta nuna damuwa a kan sake fuskantar matsaloli a zaben na Najeriya, musamman a wuraren da ta ce sam ba'a ma yi aiki da na'urarar tantanace yatsar hannu ba, tare ma da gaza samun izinin yin zabe musamman ga mutane milyan 2.3 a zaben shugaban kasa duk da cewa an tanatance su.

Shugaban tawagar Kungiyar Tarayyar Turan da suka sa ido a zaben na Najeriya a jihohin 18 Santiago Fisas ya bayyana cewa abin damuwa irin yadda aka fuskanci matsaloli na sace akwatinan zabe dama tashe-tashen hankula wanda ya ce ba abinda za'a lamunta bane.

‘Abin takaici ne yadda mutane da yawa suka rasa rayyukansu a ranar jefa kuri'a dole ne fa zabe ya kasance an yi shi cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali , ya kamata ‘yan kasa su samu damar bayyana zabinsu na siyasa a cikin kwanciyar hankalai ba tare da tsoron rayuwarsu ba. Matsalolin sun fi tsanata a jihohin Rivers da Akwa Ibom inda aka samu rahotanin tashe tashen hanklua, wannan na nuna bukatar gudanar da bincike'.

Tawagar ta sanya ido har a kan kafafen yada labarai

Tawagar ta Kungiyar Tarayyar Turan dai da ta baza jami'anta har 315 da suka sanya idannu a zaben na Najeriya inda a karon farko ta sa ido a kan kafofin yada labaru na gwamnati da masu zaman kansu da suka hada da gidajen radiyo 8 da na Telbishin guda 3 da jaridu 3. Hannah Roberts it ace matakaimakiyar shugaban tawagar da suka yi nazarin ta bayyana abinda suka gano

Nigeria Wahlbeobachter
Tawagar EU ta nuna damuwaHoto: DW/U. Musa

‘Mun gano cewar biyo bayan samaun nasarar lashe zaben shugaban kasa da jam'iyyar APC ta yi, ana samun karuwar dauko rahotani a kan al'amuran jamiyyar, abinda ya samar da dai daito da jamiyya mai mulki, to sai dai bata canza zani ba a matakin jihohin inda jamiyyar da ke mulki ke mamaye lamarin, abinda ya sabawa dokar samar da daidaito ga dukkanin yan takara'.

Tawagar za ta ci gaba da kasancewa a Najeriya har zuwa watan mayu kafin ta fitar da kamalallen rahotonta tare da ba da shawarwari a wuraren da take ganin akwai bukatar gyara.