MNA
December 4, 2018Talla
Malam Maman Barka shahararren mawakin gargajiya ne na kasar Nijar wanda Allah ya yi wa rasuwa a ranar 21 ga watan Nuwamban 2018 a birnin Yamai. Shirin na Taba Ka Lashe ya duba rayuwar wannan mawaki da kuma irin rawar da ya taka a duniyar makadan Nijar da ma kuma abubuwan da ma'abota sauraran wakokinsa da sauran jama'ar da suka yi mu'amala da shi a ciki da wajen kasar ta Nijar ke tunawa dangane da tasirin da wakokinsa suka yi a rayuwarsu.