An tabbatar da mutuwar sojojin Nijar a kauyen Bobargu
November 7, 2018Talla
Lamarin ya auku ne a kauyen mai tazarar nisan kilo mita dari da goma daga Kudu maso Yammacin kasar. Duk da ya ke hukumomin kawo yanzu ba su fito sun bayyana kungiyar da ake zargi da kai harin ba, amma a 'yan kwanakin baya bayan nan mayakan jihadi na matsa kaimi tare da kai hare haren ta'addanci a yankin. A farkon makon jiya ne, gwamnatin kasar ta tura karin sojojinta a yankin don kakkabe mayakan jihadin da tace sun yi sansani a Kudu maso Yammacin kasar mai iyaka da kasar Burkina Faso.