Shugaban Amurka ya caccaki firaministan Isra'ila
June 3, 2026
A cikin wata hira Shugaba Donald Trump na Amurka ya tabbatar da rahotannin ya caccaci Firaminista Benjamin Netanyahu na Isra'ila ta wayar tarho kan yadda yake ci gaba da fada da kungiyar Hezbollah ta Lebanon, abin da yake dagula shirin zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya, ganin Iran ta fice daga tattaunawa da Amurka, sakamakon yakin tsakanin Isra'ila da Hezbollah.
Halin da ake ciki na rikici
Wannan na zuwa lokacin da dakarun kare juyin-juya hali na Iran sun dauki alhakin harin da aka kai a kasar Kuwait, a matsayin martanin harin da Amurka ta kai kan jirgin ruwan dakon man fetur na Iran.
Hare-haren na Iran da jiragen sama marasa matukasun lalata wani bangaren na babban filin jiragen saman Kuwait, inda mutum guda ya halaka kana wasu fiye da 60 suka jikata. Ita dai Iran tana karfafa martani kan kaddarorin Amurka da ke yankin Gabas ta TSakiya, abin da ke ritsawa da kasashen da suka bai wa Amurka masauki.