A cikin shirin za a ji cewa a Jamhuriyar Nijar 'yan siyasa ne ke tofa albarkacin bakinsu kan matakin kasar Mali na ficewa daga kungiyar G5 Sahel da ma rundunar hadin gwiwa ta yaki da ta'addanci a yankin. A Saliyo kuwa, gwamnati ce tafara daukar mataki kan masu tallace-tallace da sifiku a kan hanya.