1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ambaliyar ruwa ta mamaye sansanonin 'yan gudun hijra

September 6, 2019

Amabaliyar ruwa ta barke a sansanonin ‘yan gudun hijira da suka tserewa hare-haren Kungiyar Boko Haram a jihar Borno da ke Arewa maso gabashin Najeriya tare da fargabar barkewar cututuka.

https://p.dw.com/p/3PBHP
Nigeria Flüchtlingscamp in Maiduguri
Daya daga cikin sansanonin 'yan gudun hijira a Maiduguri NajeriyaHoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

Hukumomi a jihar Borno da ke Arewa maso gabashin Najeriya sun tabbatar da ibtila'in ambaliyar ruwa a wasu sansanonin 'yan gudun hijira da ke samun mafaka a jihar, inda suka bayyana shirin kai dauki ga 'yan gudun hijira.

Likitoci masu zaman kansu sun nuna fargabar barkewar cututuka sanadiyyar ambaliyar tare da jan hankalin hukumomin jihar Borno da su gagauta daukar matakai mafi sauki don kare al'umma. 

Wannan matsalar ta barkewar ambaiyar ruwa na zuwa ne a daidai lokacin da Kungiyar Boko Haram ta hallaka mutum fiye da 50 a kasa ga makwanni biyu ciki har da sojoji, a yayin da kungiyar ke kara zafafa hare-hare a wasu sassan jihohin Borno da Yobe lamarin da ke haddasa tserewar daruruwan mutane daga garuruwansu zuwa wuraren da su ke ganin tudun na tsira ne.