1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta hukunta Belarus

Abdul-raheem Hassan
May 24, 2021

Kungiyar Tarayyar Turai ta kira jakadan kasar Belarus kan ya ba da ba'asi game da dalilan tilasta jirgin Ryanair yin saukar gaggawa a birnin Minsk, tare da neman a saki dan jaridar da hukumomi suka kama a jigin.

https://p.dw.com/p/3tsOm
In Belarus abgefangene Ryanair-Maschine
Hoto: picture alliance/dpa/ONLINER.BY/AP

Gwamnatin kasar Poland ta nuna bukatar EU ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama tsakaninta da kasar Belarus har sai an saki dan jaridar da aka kama Roman Protasevich. Kungiyar EU za ta yi nazari don cimma matsaya kan mataki na gaba don hukunta gwamnatin Belarus kan wannan mataki.

Hukumomin kasar Belarus sun tilasta jirgin fasinjan Ryanair da ya tashi daga Girka ya nufin zuwa Lithuania amma aka sauya akalar jirgin zuwa Minsk babban birnin kasar Belarus saboda dalilan na tsaro, amma daga bisani aka kama wani fitaccen dan jaridar kasar da ke cikin jirgin. Gwamnatin Belarus ta dade tana neman Roman Protasevich ruwa a jallo saboda gudanar da wata haramtacciyar kungiya.