Duk da cewa kawo yanzu ba a samu cikakkun bayanin abin da ya hadassa hatsarin ba, amma COMINAK da ke a Arewa maso yammacin Nijar ya ce ya dakatar da ayyukansa har sai an gudanar kammalallen bincike kan lamarin.
Mutane biyu sun halaka a yayin da wasu karin mutum biyun suka ji munanan raunuka a wata rugujewar kayan aiki da ta faru a kamfanin COMINAK da ke sarrafa makamashin nikiliya na Uranium a Jamhuriyar Nijar.
Hukumomin kamfanin mallakin kasar Faransa ne suka sanar da haka a yammacin ranar Lahadi.