Nijar: Minista Ben Omar ya rasu
May 3, 2020Talla
Duk da yake kawo yanzu ba a kai ga tabbatar da dalilan mutuwarsa ba, wakilin DW Hausa a birnin Niamey Mahaman Kanta ya tabbatar da rasuwar Ben Omar din wanda gabannin rasuwarsa yake rike da mukamin ministan kwadagon kasar.
A wata hira da yayi da DW a kwanakin baya, Minista Ben Omar Mohamed ya bayyana matakan da gwamnatin Nijar ke dauka wajen dakile yaduwar Corona ga ma'aikata.
Mamba a kawancen jam'iyyun da ke mulki kuma shugaban PSD Basira kana tsohon malamin jami'a, Ben Omar Mohamed ya taka muhimiyar rawa wajen tabbatar da dorewar dimukradiyar kasar.