1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matakan kariya bayan gobara a maradi

Lateefa Mustapha Ja'afar
November 11, 2021

Mahukuntan Jamhuriyar Nijar, sun kudiri aniyar daukar matakai domin kare rayukan yara kanana da ke makarantun reno wato Nursery. Wannan na zuwa ne bayan gobara ta lakume rayukan daliban firamare a jihar Maradi.

https://p.dw.com/p/42tlQ
Niger Beerdigung Schüler
Jana'izar daliban firamaren Maradi a Jamhuriyar Nijar da gobara ta lakume rayukansuHoto: Gazali Abdou

Za dai a iya cewa daukar wannan mataki ya zama tilas, bayan da a karo na biyu gobara ta lakume rayukan yarar kanana a jihar Maradi. A baya dai gobarar ta lakume rayukan yara kanana da ke makarantar reno ko kuma share fagen shiga firamare a Yamai fadar gwamnatin kasar.

Ana dai alakanta yawaitar afkuwar haduran gobara a irin wadannan makarantu da yadda azuzuwan suka kasance na zana maimakon ginin bulo ko kasa, abin da ya sanya mahukuntan na Nijar daukar matakin hana sanya kananan yara a irin wadannan azuzuwa da ke bangaren renon na makarantun firamaren kasar. 

Mutuwar daliban makarantar firamaren ta Maradi da shekarunsu suka kama daga bakwai da kuma suke daukar darasi a guda daga cikin makarantun renon da aka mayar firamare dai, ya daga hankulan al'umma tare da sanya al'hini a cikin da wajen kasar.