Najeriya ta amince da kananan matatun Mai
August 4, 2017A cewar gwamnatin Najeriyar za a fara hakan ne a karshen shekarar da ake ciki, kamar yadda shugabannin yankin na Niger Delta suka bukata. A ranar Litinin da ta gabata ne dai jagabannin yankin Niger Delta, suka yi barazanar janyewa daga tattaunawar sulhu da gwamnatin Najeriyar, muddin aka ki amince wa bukatunsu nan da ranar 1 da watan Nuwamba.
Yanzu dai gwamnatin za ta samarwa kowacce daga cikin jihohin yankin mai arzikin mai, kananan matatu biyu-biyu wadanda za su fara harkar tace man da su. Akwai ma tattaunawar da ake kai da manyan kamfanonin irinsu Shell da Chevron, don su kafa manyan cibiyoyinsu a yankin na Niger Delta.
Amincewa hakan dai, na daga cikin dabaru ne na maganta fashe bututun mai da ke faruwa a yankin da mazauna ke cewa ba sa samun amfanin arzikin da ke a yankin na su.