1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin ta'addanci ya lakume rayukan sojoji 100

Ramatu Garba Baba MNA
January 18, 2019

Sojojin Najeriya sama da 100 ne suka rasa rayukansu a sanadiyar gumurzu da 'yan ta'adda a yankin Arewa maso Gabashin kasar kamar yadda wani sabon rahoto na gungun kungiyoyin bayar da agaji ya nunar.

https://p.dw.com/p/3Bo8N
Symbolbild zur Nachricht - Streitkräfte in Kamerun zerschlagen Boko-Haram-Schule
Hoto: Getty Images/Afp/Reinnier Kaze

Rahoton ya kara da cewa, maharan da suka kai wadannan hare-haren, sun yi nasarar sace tarin makamai a yayin artabu da sojoji a yankin. Hare-hare a garuruwan Baga da Kawa a ranar 26 ga watan Disambar bara ne aka tafka asarar rayukan, inda rikicin ya kuma tilasta wa mutum sama da dubu shida tserewa daga gidajensu. An sami karuwar hare-hare na ta'addanci a makonnin da suka gabata inji rahoton.

Wani jami'in hukumar jinkai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriyan Edward Kallon, ya ce aikin isar da kayayyakin agaji na fuskantar tsaiko a dalilin yawaitar hare-haren ta'addanci da ake ci gaba da samu. Musanman ga wadanda aka tsugunar a wani sansani da ke garin Rann na jihar Borno.