An kawo karshen rikicin siyasa a Rivers?
September 18, 2025
Al'umma daga kananan hukumomin jihar ta Rivers da ke Najeriya 23 ne suka yi tururuwa, domin tarbar gwamnan nasu Sim Fubara. Tuni dai 'yan majalisar dokokin jihar da suma dokar ta-baci da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa ta shafa, suka koma bakin aiki.
Bankwana da kantoma
Ibok Ete Ibas da aka nada a matsayin kantoma, ya bar jihar tun ranar Laraba da daddare, bayan ya yi wa al'umma bayanin cewar ya cimma nasarar dukkan dalilan da suka sa aka kawo shi. Shagulgulan dakon dawowar gwamnan dai tun safiyar Alhamis, bayan ayyana dawowar gwamnan da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu bakin aiki.
A yayin zaman da suka yi bayan sun dawo bakin aiki, 'yan majalisar dokokin jihar ta Rivers sun bukaci gudanar da bincike kan shugabancin Kantoma Ibok Ete Ibas na watanni shida da kuma bukatar gwamna ya mika musu sunayen kwamishinonin da zai nada kana sun kuma sa hannu kan dokar kashe kudin gwamnati, karkashin jagorancin Martns Amaehwule.
Ko Gwamna Fubara na da kalubale a gabansa?
Dawowar Gwamna Sim Fubara kan kujerarsa ta gwamna wani abu ne kana azamar da zai sa a yanzu a matsayinsa na gwamna mai cikakken iko shi ma wani abu ne, lamarin da yanzu ke jan hankulan masu ruwa da tsaki a jihar ta Rivers. Kawo yanzu dai akwai 'yan gunaguni da ke fitowa kan yadda tsarin sababbin nade-naden da zai yi a gwamnatinsa za su kasance.