1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mafita kan matsalar tsaro a Najeriya

Uwais Abubakar Idris LMJ
July 7, 2021

Bayan kwashe shekaru masu yawa majalisar wakilan Najeriya ta yi nisa wajen aiki a kan kudurin dokar da za ta halatta kafa 'yan sandan jihohi domin shawo kan matsalolin rashin tsaro da suka adabi kasar.

https://p.dw.com/p/3wAun
Nigeria Kaduna Strategie gegen Terrorismus
A baya dai jihohin arewacin Najeriya sun yi yunkurin kafa rundunar tsaro ta jihohin yankinHoto: DW/Ibrahima Yakubu

Da alamu dai an kama hanyar kawo karshen tirje-tirje da ma tayar da jijiyar wuya, a kan wannan batu da aka kwashe lokaci mai tsawo ana ja-in-ja a kan halaccinsa ko akasin haka. Za a iya cewa batun na kafa rundunar 'yan sanda ta jihohi a Najeriyar na shirin zuwa karshe, domin kuwa majalisar wakilan kasar ta kai ga yin karatu na biyu a kan wannan kudurin doka da dan majalisa Luke Onofiok ya gabatar domin a halatta samar da 'yan san da na jihohi a Najeriyar.

Cartoon Nigeria Sicherheit Lage
Jihohin yankin Arewa maso Yamma na cikin dimuwa saboda rashin tsaro

Ko da ma dai a majalisar dattawan Najeriyar, wannan batu na samar da rundunar 'yan sandan jihohi na samun goyon baya musamman a bangaren 'yan majalisar da suka fito daga yankunan da wannan matsala ta yi Kamari. A karon farko kungiyoyin shiya-shiyya na dattawan arewacin Najeriyar da na Afenifere ta kabila Yarabawa, sun nuna goyon bayansu ga wannan yunkuri domin shawo kan matsalar tsaron. Tun a shekara ta 2019 ne dai, shugaban Najeriyar ya aika da bukatar ga majalisa ta duba wannan batu da ake ci gaba da jan kafa a kansa. Tuni shiyoyin Kudu maso Yammaci da na Kudu maso Gabashi, suka kafa nasu rundunonin tsaron saboda ta'azzara da ma lalacewar halin tsaro a Najeriyar.