Sojojin Najeriya 7 sun mutu a harin ta'addanci
October 11, 2018Talla
Rundunar tsaron kasar ce ta wallafa labarin a shafinta na Twitter, ta kuma ce akwai wasu akalla goma sha shida da suka sami rauni daga artabun. Mayakan sun far ma sansanin da ke kauyen Metele na jahar Borno kuma an kwashi akalla sa'oi bakwai ana gwabza fada a tsakanin bangarorin biyu inji sanarwar.
Wani jami'in soji da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce sojojin sun nuna kwazo a yayin da suke kokarin dakile harin na bazata sai dai mayakan sun ci karfinsu saboda yawansu. A ranar Litinin da ta gabata aka kai harin, an gano mayakan na Boko Haram sun sace wasu makamai kafin su bar sansanin baya ga wadanda suka lalata.