1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Ta'addanci

Najeriya: Matsalar 'yan gudun hijira

Lateefa Mustapha Ja'afar
November 2, 2022

Kungiyar Kare Hakkin dan Adam ta Human Rights Watch, ta bayyana cewa sama da 'yan gudun hijira dubu 200 a Najeriya da Boko Haram suka tilastawa kauracewa gidajensu na cikin halin tasku da matsin rayuwa.

https://p.dw.com/p/4IwnN
Najeriya | Borno | Maiduguri | 'Yan gudun hijira | Tasku
Halin tasku rayuwa ga dubban 'yan gudun hijira a jihar Bornon NajeriyaHoto: Gilbertson/ZUMAPRESS/picture alliance

Kungiyar ta Human Rights Watch ta bayyana haka ne cikin wani rahoto da ta fitar ta ce 'yan gudun hijirar sun shiga halin taskun ne, bayan da gwamnati ta rufe wasu sansanoninsu tare da hana kungiyoyin agaji kai musu dauki. Cikin watan Oktobar shekarar da ta gabata ta 2021 ne gwamnatin jihar Borno da ke yankin Arewa maso Gabashin Najeriyar kana makyankyasar kungiyar 'yan ta'addan ta Boko Haram da ta addabi Najeriya da makwabtanta, ta sanar da rufe dukkan sansanonin 'yan gudun hijira da ke dauke da dubban mutane tare kuma da mayar da wasunsu garuruwansu na asali.