Mahamadou Issoufou ya tattauna da dalibai
April 16, 2017Talla
Babban magatagarda na kungiyar daliban Ousseini Sambo ya ce sun tattauna da shugaba Issoufou wanda ya dauki alkawarin sake bude tattaunawa tsakanin daliban da gwamnatin,tare kuma da cewar za a dauki mataki na hukunta wadanda aka samu da laifi wajen aikata ta'adi a bangaran jami'an tsaro da ma daliban a lokacin zanga-zangar.Yanzu haka kotu ta salami wasu daliban 83 wadanda aka kama bayan tashin hankali,sai dai har yanzu ana ci gaba da tsare wasu shugabannin kungiyar daliban a gidan kurkuku.