1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bukatar Libiya ta yi da sahihin zabe

Lateefa Mustapha Ja'afar
November 12, 2021

Manyan kasashen duniya da suka halarci taron neman mafita ga Libiya a Faransa, sun bukaci Libiyan ta gudanar da sahihin zabe mai inganci.

https://p.dw.com/p/42waY
Frankreich | internationale Libyen-Konferenz in Paris
Taron nemawa kasar Libiya mafitaHoto: Yoan Valat/AP Photo/picture alliance

Taron wanda Shugaba Emmanuel Macron na Faransan ya karbar bakuncinsa, ya yi wannan kiran ne cikin sanarwar bayan taron da suka kammala a birnin Paris, inda suka yi barazanar kakaba takunkumi ga duk wanda ya yi yunkurin yin kafar ungulu ga zaben na Libiya da za a gudanar ranar 24 ga watan Disamba mai zuwa. Libiya dai ta shiga halin tasku, tun bayan da kungiyar tsaro ta NATO ta jagoranci kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar marigayi Muammar Gaddafi a shekara ta 2011.