1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu a Nijar ta Hukunta Samira Sabou

Abdourahamane Hassane
July 14, 2020

Wata kotu a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar ta yanke hukuncin daurin wata guda da kwanaki bakwai  na zaman gidan kaso ga wata 'yar jaridar wadda ke yin sharhi a kan al'amura ta intanet.

https://p.dw.com/p/3fKGC
Revisionsgericht in Niger
Hoto: DW/M. Kanta

A cikin watan Yuni da ya gabata ne aka kama Samira Sabou bayan da, dan shugaban kasar Nijar ya shigar da kara a gaban kotu a kan abin da ya kira labaran karya da ya ce Samira ta wallafa dangane da batun cinikin makamai. Cewar wani dan kasuwar ya karbi kwangilar da aka yi cin hanci a ciki da sunan dan shugaban kasar. Tuni dai da Samira ta kwashe sama da kwanaki 20 a gidan kason wacce ake tsare da ita tun 10 ga watan Yuni.