1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Jamus na karbar bakuncin taron G7

Ramatu Garba Baba
May 13, 2022

A wannan Juma'ar ake soma taron kasashen G7 inda taron zai yi nazari kan barazanar karancin abinci da duniya ke fuskanta a sakamakon yakin Rasha da Ukraine.

https://p.dw.com/p/4BEed
Deutschland Olaf Scholz und Aleksandar Vucic in Berlin
Hoto: Michael Sohn/AP Photo/picture alliance

Taron kasashen G7 masu karfin tattalin arziki na zuwa ne a daidai lokacin da yakin Rasha da Ukraine ke ci gaba ba tare da alamun ganin bayansa ba, ana ganin yakin na barazanar haifar da matsalar karancin abinci mai muni, idan ba a dauki matakin gaggawa a shawo kanta ba. Yanzu haka kasashen duniya da dama na fama da hauhawar farashin hatsi da alkama dama man girki a sanadiyar rikicin.

Taron na shekara shekara da za a kamalla a gobe Asabar ya hada kan wakilai daga kasashen Britaniya da Kanada da Italiya da Faransa da Japan da Amirka dama Tarayyar Turai ya zuwa 'yan yankin Baltic da kuma Jamus mai masaukin baki.