1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Twitter za ta ci gaba da aiki

Uwais Abubakar Idris LMJ
January 13, 2022

Kafar sada zumunta ta Tiwitter ta samu izinin ci gaba da harkokinta a Najeriya, bayan da gwamnatin kasar ta sanar da dage haramcin da ta sanya mata.

https://p.dw.com/p/45TuE
Najeriya I Haramata ayyukan kamfanin Twitter
Gwamnatin NAjeriya ta dage takunkumin da ta sanyawa kamfanin Twitter a kasarHoto: Matt Rourke/AP/picture alliance

Gwamnatin dai ta bayyana cewa, kafar sadarwar ta Twitter ta cika dukkanin sharuddan da Najeriyar ta gindaya mata. Sanar da dage haramcin da gwamnatin Najeriyar ta yi a kan dandalin sada zumuntar na  Tiwitter, na zuwa ne bayan kwashe lokaci mai tsawo ana tattaunawa tsakanin bangarorin biyu. Matakin gwamnatin ya kawo karshen dogon jira na tsamani da 'yan Najeriya suka yi na tsawon sama da watanni bakwai. Shugaban hukumar bunkasa harkokin sadarwar Internet ta Najeriya Kashifu Abdullahi ne ya sanar da dage takunkumin ga kamfanin na Twitter, cikin wata sanarwa da ya aike ga manema labarai. Tuni aka fara mayar da martani a kan lamarin. A ranar biyar ga watan Yuni na shakarar da ta gabata ta 2021 ne dai gwamnatin Najeriya ta dakatar da Twitter daga aiki a kasar, bayan da ta goge wani sako da shafin Shugaba Muhammadu Buhari ya wallafa baya ga zargin kafar da katsalanda da ma tunzura 'yan Najeriya.