1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An karkata zaben gwamnoni a Najeriya

Yusuf Bala Nayaya
March 7, 2019

Tun bayan da aka kammala zaben shugaban kasa a Najeriya da bayyana Muhammadu Buhari a matsayin wanda ya lashe hankula sun karkata kan zaben gwamnoni da wasu jihohi ake da siyasa mai zafi a cikinsu.

https://p.dw.com/p/3EbwY
Nigeria Angriff von Nomaden im Bundesstaat Plateau | Muhammadu Buhari, Präsident
Hoto: Reuters/Nigeria Presidency

An dai ga yadda siyasa ta dauki zafi a jihar Kano tsakanin 'yan takarar gwamnan jihar Kano gwamna mai ci Abdullahi Ganduje da Abba Kabir Yusuf. Haka nan jihar Kaduna inda Malam Nasir El-Rufa'i ke neman tazarce. A yankin kudanci kuwa fadace-fadace sun bayyana tun a zaben shugaban kasa.