1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta ayyana ranar makoki

Abdul-raheem Hassan
November 14, 2017

Kasar Irani ta ayyana ranar Talata a matsayin ranar zaman makoki a hukumance domin nuna jimamin mutuwar mutanen da girgigar kasa ta rufta da su a yankunan kasar masu tsaunuka da ke kan iyaka da Iraki.

https://p.dw.com/p/2nZzS
UN Generalversammlung Rohani
Hoto: Reuters/Adrees Latif

Hukumomin Iran sun kuma yi addu'a ga ga iyalan mamatan, da wadandan suka jikata da ayanzu ke gadajen asibiti sakamakon girgizar kasar. Alkaluman gwamnati na cewa adadin mutanen da suka mutu ya kai mutune 430, yayin da sama da mutane dubu 7,000 aka tabbatar suna karbar jinya.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.3 ta fi muni ne a lardunan yammacin kasar, sai dai an samu rahotannin mutuwar mutane takwas tare da jikkata mutane 500 a makociyar kasar Iraki. Ana sa ran shugaban kasar Iran Hassan Rowhani zai ziyarci yankunan da girgizar kasar ta auku.Girgizar kasa ta kashe mutane 200 a Iran