1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

HRW: Rikicin Boko Haram ya karu a Najeriya a 2018

Abdullahi Tanko Bala
January 17, 2019

A rahotonta na shekara-shekara kungiyar kare hakkin bil Adama ta duniya Human Rights Watch ta ce hare haren Boko Haram da fada tsakanin manoma da makiyaya da sace sace jama'a sun karu a arewacin Najeriya a shekarar 2018.

https://p.dw.com/p/3BkNs
Nigeria Stadt Borno State
Hoto: Getty Images/AFP/Stringer

Kungiyar ta Human Right Watch ta ce gazawar gwamnatin Najeriya na bada cikakkiyar kariya ga jama'a ya nuna wagegen gibi wajen tabbatar da tsaro.

Rahoton ya kara da cewa an kashe mutane akalla 1, 200 yayin da wasu mutanen kimanin 2000 kuma suka tagaiyara a shekarar ta 2018 a cigaba da rikicin Boko Haram da ya dauki kusan shekaru tara ana fama da shi a arewa maso gabashin kasar.

Satar mutane da hare haren kunar bakin wake da harin 'yan Boko Haram akan fararen hula sun cigaba da aukuwa duk da ikrarin sojojin gwamnati na murkushe 'yan kungiyar ta Boko Haram.