1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bai wa matasa horon kwallon kafa a Jos

Abdullahi Maidawa Kurgwi LMJ
July 10, 2019

Wani  matashi  ya bude cibiyar horas da matasa wasan kwallon kafa Najeriya, inda matasa kan sami horo don  samun kwarewa ta fanin wassan kwallon kafa da zasu rika dogaro da kai a rayuwa.

https://p.dw.com/p/3Lp9i
Gabon- African Cup of Nations - Stimmung außerhalb des Stadiums
Bayar da horo ga yara da matsa kan kwallon kafa a Jos NajeriyaHoto: picture-alliance/abaca

Wannan matashi mai suna  Adamu Babawo wanda  akafi sani da  Babawo Lecturer, ya ce tun yana karami ya ke da sha'awar  ganin kwallon kafa ta zame masa hanyar dogoro ta rayuwa, don haka ya fuskanci wassan kwallon bayan ya kammala karatu, inda yanzu haka yake da lasisin Hukumar Wasan Kwallon Kafa ta Duniya (FIFA) domin rika fitar da 'yan wasa zuwa kasashen Turai, kuma wasu daga cikinsu su kan sami zuwa kasashen na Turai  domin buga kwallon kafa. Da tallafin wannan cibiya ta horar da matasa wasan kwallo da ke Jos din, yanzu matasa masu basirar wasan kwallon kafa kan sami horo, inda sukan zamanto masu dogaro da kai a rayuwa bayan sun gama samun horon, kasancewar yanzu kwallon kafa ta zamanto babbar hanya ta samun arziki a duniya.

Ghana Project BG Ghana's viele Gesichter
Kwallon kafa: Hanyar dogaro da kaiHoto: picture-alliance/AA/M. Hossam

Wasu matasa da DW ta zanta dasu wadanda ke samun horo a cibiyar, sun bayyana kudirinsu na samun shiga manya-manyan kungiyoyin kwallon kafa da ke kasashen Turai da zarar sun kammala samun horaswar, kasancewar hatta matasan da ke da karancin ilimin zamani kan samu damar shiga cibiyar, a cewar  Shehu Romario da shi ma ke koyar da matasan kwallon kafa a cibiyar.

Masana wasan kwallon kafa a Najeriya irin su Alhaji Kwairanga na ganin babbar dama ce ta samu ga matasan Najeriya mussaman wajen fuskantar wasan kwallon kafar, domin ya zame musu hanyar dogaro da kai. Masu sharhi kan al'amuran yau da kullum na ganin ya kamata hukumomin Najeriya su nazarci hanyoyin da za'a rika sanya matasa domin neman abin kansu, kamar yadda Adamu Babawo ya yi don taimakawa matasan maimakon yadda wasunsu  kan zamanto matsala ga al'umma sakamakon rashin aikin yi.