Rikice-rikiceChadi
Hari daga Sudan ya kashe mutum 18 a Chadi
March 19, 2026
Talla
Gwamnatin Chadi ta sanar da cewa mutane 18 sun rasa rayukansu wasu da dama kuma sun sami raunuka a wani harin jirgi mara matuki da aka harbo daga Sudan wanda ya fada yammacin birnin Tine.
Garin na Tine ya na kan iyakar Chadi ne ta yammacin yankin Darfur na kasar Sudan.
Wani mai magana da yawun rundunar soji ya ce dukkan mutanen da suka mutu fararen hula ne.
Mutane a yankin sun ruwaito fashewar abubuwa guda biyu da suka fada kan masu halartar Jana'iza da kuma yara da ke wasa a kusa da wurin.