Dubban 'yan gudun hijira na fama da tsananin karancin abinci a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya a daidai lokacin da harkokin ayyukan jin-kai ke kara samun koma baya a yankin da ya sha fama da kalubalen tsaro. Kungiyoyin da ke bayar da agaji a wannan yankin na cewa akwai bukatar hankulan kasashen duniya su dawo yankin domin ceto al'umma daga mawuyacin hali da su ke ciki.