1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Neman nasara a gasar AFCON

Suleiman Babayo
January 17, 2022

Kamaru da Najeriya da Morocco sun samu tikitin tsallakawa zuwa matakin gaba a gasar AFCON da ke gudana a Kamaru.

https://p.dw.com/p/45edj
Fußball Africa Cup of Nations | Nigeria vs Ägypten
Hoto: Samuel Shivambu/BackpagePix/picture alliance

A kasar Kamaru ana ci gaba da wasannin neman cin kofin Afirka inda daga cikin kasashen 16 ake sa ran za su tsallaka zuwa matakin gaba a gasar AFCON; uku kacal ne suka samu tikitin ciki har da Kamaru mai masaukin baki da Najeriya da kuma Morocco da maki shida kowaccen su a wasanni. Amma sauran kasashen na jiran wasansu na uku domin sanin makomarsu.

Ga kuma yadda wasannin lig na Jamus da ake kira Bundesliga da aka kara a karshen mako ya kasance:

Wolfsburg                   0     Hertha BSC            0

Union Berlin               2     Hoffenheim             1

Stuttgart                     0     RB Leipzig             2

Mainz 05                    1     Bochum                 0

Borussia M'gladbach 1     Bayer Leverkusen  2     

Serbien | Ankunft Novak Djokovic am Flughafen in Belgrad
Dan wasan tennis Novak Djokovic Hoto: Christopher Pike/REUTERS

Bayan da aka shafe kwanaki goma ana kai kawo tsakanin shaharraren dan wasan Tennis Novak Djokovic da gwamnatin Australiya, kotu ta yanke hukuncin tasa keyar dan wasan bisa samun shi da laifin karya dokokin da suka shafe tanadin allurar rigakafin COVID-19. Kuma mai yiwuwa ma za'a dakatar da shi daga karawa a wasan Australiyan Open na tsawon shekaru uku masu zuwa. Wannan matakin dai ya dakusar da yanayin annushuwan da jama'a kan shiga a watan Janairun kowace shekara don dokin zuwan gasar na Tennis da aka fi sani da Australiyan Open.